31/12/2025
KUNGIYAR CI-GABAN GARIN DIKKE TA KARRAMA SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR FUNTUA HON AUDU GOYA DA HON BARA'U YUSUF MAIKWAI DIKKE....
Kungiyar Ci gaban Garin Dikke, Mai Suna Dikke Consultative Forum DCF
Dake Karamar Hukumar Funtua Ta Karrama Shugaban Karamar Hukumar Funtua Hon Abdulmutallab Jibrin Sulaiman Goya da Hon Bara'u Yusuf Maikwai Dukke Supervisory Councilor Health Department Funtua Local Government Council Da Lambobin Girmamawa bisa kyakkyawan Jagoranci da Cigaban karamar Hukumar Funtua.
Kungiyar Dukke Consultative Forum (DCF) ta karrama Mai Girma Hon. Abdulmutallab Jibrin Sulaiman Goya, Shugaban Karamar Hukumar Funtua, da kuma Hon. Bara’u Yusuf Maikwai, Supervisory Councilor mai kula da Sashen Lafiya na Karamar Hukumar Funtua, da Lambobin Yabo na Girmamawa.
Wannan karramawa ta zo ne bisa gagarumin ƙoƙari, jajircewa da sadaukarwar da suke yi wajen inganta ci gaban Karamar Hukumar Funtua, musamman a fannoni daban-daban na raya kasa, kula da jin daɗin al’umma, bunkasa harkokin lafiya da tallafa wa marasa ƙarfi a kowane lokaci.
Shugabancinsu ya kasance abin koyi, domin suna ci gaba da nuna nagartaccen jagoranci, gaskiya da kishin al’umma, tare da ɗaukar manufofi masu alfanu da ke ƙarfafa ci gaba mai ɗorewa ga al’ummar Funtua baki ɗaya.
Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙara musu hikima, lafiya da ƙarfin guiwa, Ya tsawaita musu rai cikin hidima, Ya albarkaci dukkan ayyukansu, tare da ba su ikon cigaba da jagorantar al’umma bisa adalci da gaskiya domin ci gaban Karamar Hukumar Funtua da ƙasa baki ɗaya.
Ubangiji Allah yasa Alkairee 🙏
